News
Ƴan Najeriya na Shan Baƙar Wahala a ƙarƙashin Gwamnatin Yanzu -Inji Sheikh Gumi
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Malamin Addinin Musulunci a Najeriya Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana rashin jindaɗi na yadda Matsalar Tattalin Arziki da na tsaro ke cigaba da addabar Kasar.
Gumi, wanda ya kasance tsohon Soja, ya jaddada irin yadda ƴan Najeriya ke cigaba da shan wahala sakamakon waɗannan matsaloli a Ƙasar.
A wata tattaunawa da Majiyar mu a ranar Talata, Gumi ya koka na yadda ƴan Najeriya da yawa basa iya ciyar da kansu a yayinda Farashin Kayayyaki ke cigaba da tashin gwauron zabi a Kasuwanni.
Dayake jawabi akan kai harin Jirgin Ƙasa na Abuja-Kaduna, Malamin Musuluncin ya addu’ar gaggawar sakin waɗanda ake riƙe dasu a wajen ƴan bindiga.
Gumi yayi kira ga ƴan Najeriya dasu zama masu haɗin kai a yayin da Babban Zaɓen 2023, ke cigaba da matsowa, domin samar da ingantacciyar Gwamnati da zata magance wahalhalun da ƴan Najeriya suke sha a ƙarƙashin wannan Gwamnatin.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
