Sports
Dan Najeriya ya zama kocin tawagar ‘yan wasan kwallon Amurka
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
An naɗa tsohon mai bugawa Najeriya, Michael Nsien, a matsayin kocin tawagar ‘yan wasan Amurka ajin matasa ‘yan kasa da shekara 16.
An sanar da naɗin Nsien a shafukan wasanni na Amurka.
Nsien mai shekara 41 haifafen yankin Tulsa ne da ke jihar Oklahoma ta Amurka, kuma yana cikin tawagar ‘yan Super Eagles ajin kasa da shekara 23 da suka gaza zuwa gasar Olympic ta 2004 a Athens.
Dan kwallon na da kwarewa sosai na tsawon shekara 12 da ya shafe yana horar da ‘yan wasa a jiharsa kafin ya samu lasisin UEFA.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
