News
An Fara Samun Wutar Lantarki A Wasu Daga Cikin Jihohin Arewacin Najeriya

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Bayan daukar kwanaki goma 11 a jere babu wutar lantarki a sassan jihohin Arewacin Najeriya a yanzu haka hasken Wutar lantarkin ya Fara dawowa zuwa wasu jihohin.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewar an fara dawo da wutar ne da misalin karfe 7:20 na daren ranar laraba a wasu jahohin Arewa maso tsakiya da Arewa maso gabas.
ta ce mazauna garin Jos babban birnin jihar Filato, Bauchi, Gombe da Benue sun tabbatar mata da dawo musu da lantarkin.
A yanzu dai za’a iya cewa babu labarin da Al’umma Arewacin Najeriya suke sanji saina dawowar wutar lantarki.