Connect with us

News

An Gano Motar Da A Ka Sace A Gidan Gwamnatin Kano

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta bayyana cewa ta samu nasarar gano motar Toyota Hilux da aka sace daga ofishin mataimakin gwamnan jihar.

A cewar rahoton da ofishin mataimakin gwamnan ya samu daga ‘yan sanda, an gano motar ne da safiyar Laraba bayan bincike mai zurfi na hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro.

Advertisement

Tsohon Ministan Sufuri Rotimi Amaechi Ya Zargi Wasu Jiga-jigan Gwamnati Da Hana Sauya Tsarin Zabe

An kuma kama wanda ake zargi da satar motar, wanda aka bayyana cewa direba ne a gidan gwamnatin jihar. Yanzu haka yana hannun ‘yan sanda yana taimakawa wajen bincike.

Ofishin mataimakin gwamnan ya jinjinawa yadda rundunar ‘yan sanda ta gaggauta daukar mataki da kuma kwararrun hanyoyin da ta bi wajen gano motar.

Advertisement

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu, ya fitar, ofishin ya bayyana cewa lamarin “cin amana ne daga direban da aka kama.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending