Connect with us

News

Zargin Ɓata Suna: Gbajabiamila Ya Kai Adeyemi Kotu, Ya Nemi Diya Ta Naira Biliyan 15.2

Published

on

FB IMG 1784253147794

Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan Frins Adeniyi Adeyemi Matthew, bisa zargin ɓata masa suna.

A cikin ƙarar, Gbajabiamila ya nemi kotu ta umarci Adeyemi ya biya shi diyyar Naira biliyan 15.2, yana mai cewa kalaman da ya yaɗa a kansa sun jawo masa zubewar mutunci da martaba.

Yan Bindiga Sun Tilastawa Mazauna Ƙauyukan Tserewa Daga Gidajensu A Benue

Ya ce zargin da aka yi masa na neman cin hanci ƙarya ce, kuma ba ta da wata hujja. Saboda haka, ya roƙi kotu ta tilasta wa wanda ake ƙara ya janye kalaman tare da bayar da uzuri a bainar jama’a.

Rahotanni sun nuna cewa Adeyemi, wanda ake zargi da bayyana kansa a matsayin Darakta Janar na wata hukuma mai suna PFIPC, ya taɓa zargin Gbajabiamila da yunƙurin amfani da hukumomin tsaro a kansa. Haka kuma ya yi iƙirarin cewa marigayi Babatunde Tanimola ya kasance mai shiga tsakaninsu.

Sai dai Gbajabiamila ya musanta dukkan waɗannan zarge-zarge, yana mai cewa ƙirƙirarru ne kuma ba su da wani tushe.

Advertisement

Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, Adeyemi bai fito da wata sanarwa a hukumance ba game da ƙarar da aka shigar a kansa.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending