Connect with us

News

Jami’an Yansanda Sun Cafke likitoci Kan Zargin Safarar Mutane Da Cire Musu Ƙoda

Published

on

c48e2f50 495e 4787 8667 72d32b04cadf 1787991341317

Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta cafke wasu mutane huɗu, ciki har da likitocin ƙoda biyu, bisa zargin hannu a wata ƙungiyar safarar mutane da cire sassan jikin bil’adama ba bisa ƙa’ida ba a Jihar Nasarawa.

Waɗanda aka cafke sun haɗa da Emmanuel Ode, mai shekaru 23; Dakta Benjamin Oyime, mai shekaru 48, likitan ƙoda kuma mai ba da shawara a Asibitin Wellington da ke Life Camp, Abuja; Dakta Daniel Otukpa, mai shekaru 53, shi ma likitan ƙoda kuma Mukaddashin Daraktan Ayyukan Kula da Lafiya na asibitin; da David Idoko, mai shekaru 25.

KADUNA: Jami’an Ƴansanda Sun Tarwatsa Sansanonin Ƴan Bindiga A Makarfi

Jami’an Special Tactical Squad (STS) ne suka kama mutanen a ranar 19 ga Agustan 2026, yayin wani samame da suka gudanar a Auta Balifi, cikin Ƙaramar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa, bayan samun bayanan sirri kan ayyukan ƙungiyar.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Ani Iniedu, ya ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun mayar da hankali ne kan matasa masu rauni da kuma waɗanda ke fama da matsalar kuɗi a Nasarawa da kewaye.

A cewar ’yan sandan, Ode ya amsa cewa yana ɗaukar waɗanda abin ya shafa ne ta hanyar yaudararsu. Rundunar ta ce a ranar 24 ga Afrilun 2026, ya kai wani matashi mai suna Samuel Ezekiel, mai shekaru 22, zuwa Asibitin Wellington da ke Abuja, inda ake zargin an cire masa ƙoda tare da biyan sa dala 1,250, wato kusan Naira miliyan 1.7.

Advertisement

Rundunar ta ce wani mutum na biyu da ake zargin ya shaida cewa Ode ne ya yaudare shi a shekarar 2022 zuwa wani asibiti, inda aka cire masa ƙoda sannan aka biya shi Naira miliyan bakwai.

’Yan sandan sun kuma ce bincike ya gano cewa ana amfani da takardun bogi, ciki har da NIN, takardun haihuwa, takardun bayyana shekaru, takardun rantsuwa da kuma takardun amincewa, domin sauƙaƙa aikata laifukan.

Rundunar ta ce an ƙwato wasu kayayyaki da ake zargin an saya da kuɗin da aka samu daga aikata laifin, yayin da bincike ke ci gaba da gudana domin cafke wasu mutane da ake zargin suna da alaƙa da ƙungiyar.

 

 

 

Advertisement

TRT AFRIKA

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending