News
An Yi Wa Malamar Jami’ar FUT Yankar Rago A Gidanta Da Ke Minna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
An yi ma wata malamar jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya (FUT), da ke Minna a jihar Neja, Dakta Sherifat Funmilola Adefolalu, yankan rago a gidanta da ke Minna ranar Lahadi.
An gano ta kwance a mace a cikin gidanta da ke unguwar Bbaiko a Minna.
An kona zauren majalisar dokokin jihar Ribas Bayan Barazanar Tsige Gwamna
An fahimci cewa ‘yan uwa da abokan arzikinta sun yi ta ƙoƙarin nemanta ta wayar tarho amma ba su sameta tun da safiyar ranar Lahadi.
A lokacin da wasu da suka damu da cewa ba su ji ɗuriyarta, sun je gidanta domin neman ta kwatsam sai suka tarar da malamar a tsangayar koyar da ilimin Biochemistry kwance cikin jini.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun, ya tabbatar wa LEADERSHIP cewa wasu abokanta sun je gidanta nemanta sakamakon cewa sun kasa samunta a waya.
“Abun takaici, a lokacin da masu ziyarartar nata suka shiga cikin gidanta, sun risketa kwance cikin jini ga kuma raunuka a sassan jikinta.”
Ya ce, wasu wuƙaƙe guda biyu ɗauke da jini a jikinsu da ake zargin da su ne makasan suka yi amfani wajen daddaɓa mata an samesu a inda lamarin ya faru.
PPRO ya ce an ɗauki gawar mamaciyar zuwa asibitin IBB inda a nan ma likita ya tabbatar da cewa ta mutu, ya ƙara da cewa tunin aka ƙaddamar da bincike domin gano makasan, ya ba da tabbacin cewa za su yi duk mai yiyu domin kamo makasan.
Shi ma shugaban ƙungiyar ASUU reshen jami’ar FUT Minna, Dakta Bolarin Gbolahan, ya tabbatar da kisan da aka yi wa mambarsu.
Dr Gbolahan ya koka kan cewa kusan kowa mako yanzu sai an yi garkuwa da mambobinsu a Keffi, “Rayuwar mu cikin hatsari ba mu iya barci da ido biyu. Dole a dauki mataki kafin dukkanin mu ya mu ƙare.”
