News
An kona zauren majalisar dokokin jihar Ribas Bayan Barazanar Tsige Gwamna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
An kona zauren majalisar dokokin jihar Ribas Bayan Barazanar Tsige Gwamna
Wannan ci gaban ya zo ne a daidai lokacin da ake ta rade-radin shirin tsige Gwamna Similanayi Fubara.
Daily Trust ta rawaito cewa maharin sun samu shiga majalisar dokokin ne a daren ranar Lahadi inda suka kona ta.
Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Yi Barazanar Kauracewa Ganawa Da Gwamnatin Tarayya a Gobe Litinin
Rahotanni na nuni da cewa daukin gaggawar da jami’an kashe gobara suka yi ne ya hana gobarar bazuwa a harabar majalisar baki daya.
Kokarin da aka yi na zantawa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, SP Grace Iringe Koko ya ci tura a lokacin da ake gabatar da wannan rahoto.
An tsaurara matakan tsaro a harabar ginin yayin da jami’an kashe gobara ke fafatawa don shawo kan gobarar.
A wani labarin kuma Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Yi Barazanar Kauracewa Ganawa Da Gwamnatin Tarayya a Gobe Litinin
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
