Connect with us

News

Tsadar Rayuwa: Jama’a Sun Daka Wa Motar Dangote Wawa A Katsina

Published

on

DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO

 

Advertisement

Jama’ar gari a Jihar Katsina sun daka wa wata motar kamfanin Dangote wawa, inda suka yi awon gaba da kayan abincin da take dauke da su.

Hakan ta faru ne a yayin da matsin rayuwa da tsadar kayan masarufi a Najeriya suka kai makura, inda kudin buhun masara ya kusa ninka mafi karancin albashi.

Advertisement

Jami’an Rundunar Sojin Saman Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Yin Garkuwa Da Mutane A Kano 

A bidiyon wasoson da ke yawo a kafofin sada zumunta, an ga maza da mata da kananan yara suna daukar buhunan kayan abinci suna awon gaba da su daga babbar motar da ke kan babbar hanya.

Wasu daga cikin mutanen kuma suna kokawar daukar buhunan abincin, da ake zargin za a kai kasar Jamhuriyar Nijar ne.

Advertisement

Amma a sanarwar kamfanin da ke tabbatar da aukuwar lamarin, kamfanin na Dangote ya musanta cewa Nijar zai kai kayan abincin.

Aminiya ta ruwaito cewa a shekarar da ta gabata ne Najeriya ta rufe iyakarta da Nijar sakamakon hambarar da Shugaba Mohamed Bazoum da sojojin kasar suka yi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending