Connect with us

News

Babbar Magana: Za a yanke wutar lantarki a Fadar Shugaban Ƙasa da CBN saboda bashi

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Kamfanin rarraba wutar lantarki, wato Abuja Electricity Distribution Company, ya ba da sanarwar zai yanke wutar lantarki a Fadar Shugaban Ƙasa da Babban Bankin Nijeriya (CBN) da wasu ma’aikatu da hukumomi 85 na Gwamnatin Tarayya saboda bashin kuɗin wuta da ya kai sama da Naira biliyan 47,195 ya zuwa Disamban 2023.

Advertisement

AEDC ya bayyana haka ne a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, 19 ga Fabrairu, 2024.

Tsadar Rayuwa: Jama’a Sun Daka Wa Motar Dangote Wawa A Katsina

AEDC ya bayyana cewa, “Hukumar Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) ta bada wa’adin kwana 10 ga ma’aikatu da hukumomin gwamnati 86 kan su biya bashin kauɗin wuta, N47.1bn da ake bin su ko kuma su fuskanbci hatsarin yanke musu wuta.

Advertisement

“Bayan cikan wa’adin kwana 10 wanda zai ƙare ran Laraba, 28 ga Fabrairu, 2024, AEDC zai fara yanke wutar duk wanda bai biya bashin da ke kansa ba.”

Sauran wuraren da lamarin ya shafa sun haɗa da Barikin Babban Hafsan Tsaro, Ma’aikatar Birnin Tarayya, Ofishin Gwamnatin Jihar Neja da ke Abuja.

Advertisement

Sai kuma Ƙaramar Ma’aikatar Fetur, Fadar Shugaban Ƙasa, Ma’aikatar Ilimi, Babban Bankin Nijeriya, Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya da dai sauransu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending