Connect with us

News

Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Published

on

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Sanata, Ibrahim Shekarau, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP a hukumance.

A wata wasiƙar murabus da ya aike a yau Lahadi, 19 ga Afrilu, 2026, zuwa ga shugabannin jam’iyyar a unguwar Giginyu da ke ƙaramar hukumar Nassarawa, Shekarau ya bayyana cewa ya yanke wannan shawara ne bayan tattaunawa mai zurfi da mambobin ƙungiyarsa ta siyasa.

Advertisement

Motar Tifa Ta Murƙushe Mutum 3 Har lahira ‎

Tsohon gwamnan ya ce ya shirya komawa wata jam’iyya domin ci gaba da harkokinsa na siyasa, duk da cewa bai bayyana sunan sabuwar jam’iyyar ba a cikin wasiƙar.

Advertisement

Sai dai ya yaba da shugabannin jam’iyyar ta PDP, inda ya bayyana su a matsayin nagartattu, tsu.

An kuma aika kwafin wasiƙar ga shugaban PDP na jihar Kano da kuma na ƙaramar hukumar Nassarawa, a matsayin sanarwa a hukumance kan matakin da ya ɗauka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending