Connect with us

Uncategorized

An Daura Auren Kamaldeen Adamu Da Khadija Samisu A Garin Kura

Published

on

IMG 20260731 144726 221

An daura auren Kamaldeen Adamu, ɗan Alhaji Adamu Yusuf Ganga, da amaryarsa Khadija Samisu Muhammad, ‘yar Alhaji Saminu Muhammad Kura, a ranar Juma’a, 31 ga Yuli, 2026, a Masallacin Juma’a na Umar Bin Abdul’aziz JIBWIS, da ke Kofar Arewa a garin Kura, Jihar Kano.

Bikin daurin auren ya samu halartar malamai, ‘yan uwa, abokai da sauran masu fatan alheri daga sassa daban-daban, waɗanda suka taru domin shaida wannan muhimmin lamari tare da yi wa ma’auratan addu’ar samun zaman lafiya da albarka.

Gwamnatin Kano Ta Kama Mutum Biyu Bisa  Zargi Da Sayar Da Filayen Gwamnati A Rimin Zakara

An gudanar da daurin auren cikin natsuwa da bin koyarwar addinin Musulunci, inda aka roƙi Allah Madaukakin Sarki Ya sanya albarka a rayuwar sabbin ma’auratan, Ya ba su zaman lafiya, soyayya, fahimtar juna da zuri’a ta gari.

Mahalarta bikin sun taya iyalan Alhaji Adamu Yusuf Ganga da na Alhaji Saminu Muhammad Kura murnar wannan farin ciki, tare da yi musu fatan alheri da ɗorewar zumunci tsakanin iyalan biyu.

Allah Ya sanya wannan aure ya zama mai albarka, Ya kuma sa ya kasance mafarin rayuwa mai cike da farin ciki, rahama da ci gaba ga ma’auratan. Ameen.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending