News
Za Mu Rufe Jami’o’i Nan Da Kwanaki Bakwai —SSANU
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Najeriya (SSANU) Mohammed Ibrahim ya ce za su tafi yajin aiki idan gwamnati ta ki biya musu bukatunsu nan da kwanaki bakwai.
Ya bayyana cewa za su shiga yajin aikin ne tare da wasu kungiyoyin ma’aikatan jami’o’i biyu na kasar nan
Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ –Kashim Shettima
Ibrahim ya ce, sun ba Gwamnatin Tarayya wa’adin kwanaki bakwai, daga ranar Litinin 4 ga Mayu, 2024
Da ake hira da shi a gidan talabijin na Channels TV ranar Lahadi, ya yi barazanar cewa kungiyoyin za su rufe jami’o’in gaba daya, idan gwamnatin ba ta yi wani abu ba a karshen wa’adin.
“Mu ne masu kula da harkokin tsaron jami’o’in da gudanar da mulki da kula da likitoci da dakunan kwanan dalibai da da wutar lantarki da tafiyar da komai bayan koyarwa, don haka da zarar mambobinmu sun daina aiki, babu wata jami’a da za ta iya aiki a Najeriya.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
