Connect with us

News

Nijar ta hana fitar da man da aka tace a ƙasar zuwa ƙasashen waje

Published

on

Mohamed Bazoum

Daga kabiru basiru fulatan 

 

 

 

Gwamnatin Nijar ta haramta fitar da man fetur da aka tace, kamar yadda gwamnatin kasar ta bayyana a cikn wata sanarwa a ranar Laraba, a wani mataki na tabbatar da wadatuwar man a ƙasar.

Majalisar dokoki ta dakatar da ciyamomin Ƙananan Hukumomi 2 a Kaduna

Advertisement

 

Tun a farkon watan Mayu Nijar ta rage yawan man da take fitarwa da kashi 75 domin ƙara yawaitar man a cikin ƙasa yayin da farashn ɗanyen mai ke ƙara tsada a kasuwar duniya wanda yaƙin Ukraine ya haddasa.

 

Ma’aikatar kula da cinikayya da albarkatun man fetir ta ƙasar ta ce matakin zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Yuni.

 

Nijar na cikin sabbin ƙasashen Afirka da ke tace mansu domin amfann ƴan ƙasa a ƙaramar matatar mai da ke tace ganga 20,000 a rana.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending