Connect with us

News

Daliban Kaduna 701 ba za su rubuta jarrabawar WAEC ba

Published

on

Daga maryam bashir musa

 

 

 

Dalibai 701 daga jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya ba za su zana jarrabawar kammala sakandire ta WAEC ba saboda rashin ba su damar biyan kudaden da ya kamata su biya.

Buhari ya bukaci tinubu ya janye takarar da yake na shugabancin kasa a jam,iyyar Apc

Advertisement

 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa daliban, wadanda suka fito daga makarantun sakandire daban-daban a jihar an i ba su damar sanya makinsu na makaranta a shafin hukumar da ake shirya jarrabawar kammala karatun sakandiren.

 

Ko da yake, hukumar daga bisani ta yi kira ga makarantun da abin ya shafa a kan cewa za a ƙara buɗe shafin domin su sanya makin nasu.

 

Makarantun da abin ya shafi ɗalibansu sun haɗa da Government Secondary School Kuse, wadda ɗalibanta da ke ajin karshe 290 abin ya shafa.

Advertisement

 

Sai Government Secondary School Independence Way Kaduna, mai ɗalibai 150 da Government Secondary School Kagarko mai dalibai 110 da kuma Government Senior Secondary School Iddah mai dalibai 100.

 

Sauran sun hadar da Al-Bahmeen Academy, Kaduna mai dalibai takwas da Kalhyatu AbdulRahman Bin Auf Academy, Jere mai dalibai 15 da Great Panaf Schools Kaduna mai dalibai 13 da ECWA Secondary School, Kubacha mai dalibai 10 sai kuma Government Secondary School Mato mai dalibai biyar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending