Connect with us

News

Zan nemi takarar shugaban kasa idan har PDP ta ba Kudu tikiti – Peter Obi

Published

on

FB IMG 16437580563128123
Spread the love

Daga

muhammad muhammad zahraddin

Tsohon gwamnar Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya, Peter Obi, ya ce zai tsaya takarar shugabancin kasar idan har jam’iyyarsa ta PDP ta bai wa kudu tikitin.

Advertisement

Mista Obi, wanda ya yi wa PDP takarar mataimakin shugaban kasa a 2019, tare da Atiku Abubakar, ya bayyana hakan ne a sakon da ya wallafa a tuwita ranar Talata.

“Eh tabbas zan tsaya takarar shugabancin Najeriya domin samun damar yi wa kasata hidima a matsayin shugaban kasa, idan har jam’iyyata ta PDP ta kai tikitin kudu, amma ko an bayar da dama ga kowane bangare na kasar,

‘Yan Najeriya za su ji daga gareni,” ya rubuta a shafin Tuwita.

Advertisement

Sanarwar Mista Obi na zuwa ne kasa da awa 24 bayan da gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Tambuwal ya shelanta aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasar karkashin jam’iyyar PDP.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *