Kamfanin mai na NNPC a Najeriya ya ce yana da wadataccen man fetur don rarrabawa a faɗin ƙasar.
An shafe kusan mako biyu ana wahalar man fetur a sassan Najeriya.
A wata sanarwa da NNPC ya fitar ya jaddawa ƴan Najeriya cewa akwai isasshen man fetur kuma kamfanin na aiki da abokan hulɗarsa don tabbatar da cewa ya isa a kowane ɓangare na ƙasar.
NNPC ya kuma yi kira ga ƴan Najeriya su ci gaba da haƙuri yayin da ake ƙoƙarin ganin abubuwa sun koma daidai.