News
UEFA ta dage wasan karshe na Champions League daga Russia zuwa Faransa
Daga kabiru basiru fulatan
Hukumar kwallon kafa ta nahiyar turai UEFA ta dage wasan karshe na maza na gasar cin kofin zakarun turai Champions League na shekarar 2021/2022 daga kasar Russia zuwa Faransa.
Hakan na zuwa ne bayan wani zama da masu ruwa da tsaki na hukumar suka gudanar a ranar Juma’a 24 ga Fabrairun 2022 da muke ciki.
UEFA ta ce dage wasan ya biyo bayan yadda matsalar tashin hankali ke ci gaba da wakana tsakanin Russia da Ukraine.
Wasan karshen dai an tsara gudanarwa a birnin Saint Petersburg, wanda kawo yanzu za a gudanar a filin Stade de France da ke kasar Faransa a ranar Asabar 28 ga Mayun 2022.
Zuwa yanzu dai ana ci gaba da musayar wuta tsakanin kasashen Russia da Ukraine da sakamakon haka ake ci gaba da dage wasanni da dama a kasashen biyu.
-
Uncategorized6 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News22 hours ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
