Connect with us

News

Ɓangarorin Da Amurka Da Iran Suka Gaza Cim Ma Matsaya Cikin Yarjejeniya

Published

on

iran (1)
Advertisements
ads

An kammala zagayen farko na tattaunawa kai-tsaye tsakanin Amurka da Iran don kawo ƙarshen yaƙin Gabas ta Tsakiya a Switzerland ranar Litinin, bayan zaman sa’o’i 18 a gaɓar Tafkin Lucerne, wanda Pakistan da Qatar suka shiga tsakani. Ɓangarorin biyu sun bayyana tattaunawar a matsayin mai ma’ana kuma sun amince da ɗaukar kwanaki 60 don cim ma yarjejeniya ta ƙarshe.

Amma cikin sa’o’i bayan tafiyar wakilan, gwamnatocin ƙasashen biyu sun bayyana saɓani da juna a bainar jama’a kan kusan dukkan manyan batutuwa, tun daga ko za a bar masu sanya idanu na Majalisar Dinkin Duniya su shiga cibiyoyin nukiliya na Iran, zuwa ga wanda zai kula da yadda za a yi amfani da biliyoyin kadarorin Iran da aka saka wa takunkumi. Taƙaddamar ta nuna irin nisan da Washington da Tehran ke da shi, duk da cewa suna fafatawa da kuma tsawon kwanaki 60 don guje wa komawa yaƙi.

Farashin Fetur Ya Ki Sauka A Najeriya Duk Da Faduwar Farashin Ɗanyen Mai A Kasuwannin Duniya

Duba wuraren sarrafa Nukiliya

Babban rashin jituwar ta shafi binciken nukiliya. Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ya faɗa a ranar Litinin cewa, Iran ta amince ta bar masu binciken Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) su koma ƙasar, yana mai bayyana hakan a matsayin babban mataki na hana Tehran mallakar makamin nukiliya.

Jami’an Iran sun yi watsi da wannan bayanin nan da nan, inda mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje Esmaeil Baqaei ya ce babu wani shiri na ziyarar IAEA kuma babu wani sabon alkawari kan binciken.

Advertisement

Shugaban Amurka Donald Trump daga baya ya dage cewa Iran ta amince “100%” kan za a duba kuma ya yi gargaɗin cewa, zai soke tattaunawar idan ba haka ba ne. Ya kuma ce masu binciken za su shiga Iran “a lokacin da ya dace.”

 

Kuɗaɗen da aka sanya wa takunkumi

Ɓangarorin biyu kuma suna cikin rashin jituwa kan yadda za a saki kadarorin Iran da aka saka wa takunkumi da kuma amfani da su a ƙarƙashin duk wani shiri da ya taso.

Gwamnan Babban Bankin Iran Abdolnaser Hemmati ya ce matsayin kashi na farko na kuɗaɗen ya dogara ne a kan fahimtar juna ta 2023 da aka yi da Washington game da kayayyaki da magunguna masu muhimmanci, kuma ya ce Iran ba ta da alhakin sayen kayayyakin noma na Amurka.

Ya ƙara da cewa Iran za ta iya sayen masara, alkama ko waken soya na Amurka idan farashi da inganci na da kyau, amma ya jaddada cewa fifikon Tehran shi ne samun damar ajiyar kuɗin ƙasashen waje da sassauci a kan kashe kuɗi.

Advertisement

Duk da haka, Shugaban Amurka, Donald Trump, ya dage cewa duk wani asusun Iran da ba a daskarar ba za a sanya shi a cikin asusun ajiyar kuɗi na Amurka, kuma ana amfani da shi musamman don sayen kayayyakin noma na Amurka, yana mai bayyana cewa shirin zai amfani manoman Amurka da kuma tabbatar da sa ido kan kashe kuɗin Iran.

Jami’an Iran sun mayar da martani. Kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje Esmaeil Baqaei ya ce shawarwarin shigar da kaya zuwa Tehran daga Amurka za su dogara ne a kan “farashi da inganci,” yayin da jakadan Iran a Geneva, Ali Bahreini, ya ce Iran ce kaɗai za ta yanke shawara kan yadda za a yi amfani da kadarorinta.

Masu shiga tsakani na Iran sun ambaci kimanin dala biliyan 12 a cikin asusun da ake sa ran za a saki, ko da yake, Washington ba ta tabbatar da hakan ba. Kiyasi mai zurfi ya nuna cewa Iran tana da dubban biliyoyin daloli na kadarorin da aka saka wa takunkumai a ƙasashe da dama, inda tattaunawar da ake yi a yanzu ta mayar da hankali kan kashi na farko.

 

Mashigar Teku ta Hormuz

An sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a makon da ya gabata don sake buɗe mashigar teku mai muhimmanci nan-take tare da tabbatar da cewa ba za a dinga biyan kuɗin shiga ba na tsawon kwanaki 60, amma yarjejeniyar ta wargaje cikin sauri.

Advertisement

Dakarun Juyin-Juya-Hali na Iran sun ce tana sake dawo da taƙaita wucewar, tana mai ambaton “laifukan” Isra’ila a Lebanon da gazawar Amurka wajen cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta. “Kada jiragen ruwa su kusanci mashigar; in ba haka ba, amincinsu zai kasance cikin hatsari,” in ji ta.

Babban mai shiga tsakani na Iran Mohammad Bagher Ghalibaf ya bayyana a ranar Lahadi cewa, Tehran ta amince da samun hanyar sadarwa game da wucewar jiragen ruwa a Mashigar Teku ta Hormuz don gujewa afkuwar lamari marar kyau.

Da yake tsayawa a Oman a kan hanyarsa ta komawa gida daga tattaunawar Switzerland, Ghalibaf ya bayyana cewa: “Mashigar Hormuz ba za ta sake koma wa yanayinta na kafin yaƙi ba, kuma Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta kula da mashigar, bisa ga dokokin ƙasa da ƙasa.”

Duk da haka, rundunar sojin Amurka ta ce dakarunta suna “nan kuma suna cikin shiri” a yankin, kuma suna aiki don tabbatar da bin yarjejeniyar. Ta rawaito cewa jiragen ruwa 55 na kasuwanci sun ratsa mashigar a ranar Asabar kuma ta ce hanya mai tsaro na ci gaba da “kasancewa”.

A halin yanzu, shugaban Amurka Donald Trump ya dage cewa mashigar tekun za ta kasance ba tare da biyan kuɗin shiga daga Iran a lokaci da kuma bayan tattaunawar na tsawon kwanaki 60.

Haɓaka makamashin uranium

Advertisement

Wani mamba na tawagar tattaunawa ta Iran ya ce an cim ma daftari a rubuce kan “watsi da takunkumi na wucin gadi kan man fetur da albarkatun mai.” Sai dai, jami’ai a ɓangarorin biyu sun ce bunƙasa makamshin Iran ya kasance batun da ya fi sarƙaƙiya wanda kuma ba a warware shi ba, kuma ya zama babban abu mai hatsari da ke cikin tattaunawar.

Yayin da ake ci gaba da tattaunawar a ranar Lahadi, Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya dage cewa Tehran ba za ta yi sassauci kan haƙƙinta na nukiliya ba, yana mai cewa: “Ba za mu taɓa ja da baya daga haƙƙin haɓaka uranium ba, kuma ɗayan ɓangaren ma an tilasta masa ya yarda da hakan,” a cewar kafofin watsa labarai na gwamnati.

Shugaban Amurka Donald Trump ya mayar da martani a wata hira da Fox News jim kaɗan bayan haka, yana gargaɗin Pezeshkian da ya “duba abin da yake faɗa” kuma ya yi barazanar “ƙwace Iran,” kalaman da suka nuna rashin tabbas da ke tattare da tattaunawar.

Iran tana tunkarar tattaunawar cikin taka-tsan-tsan, idan aka yi la’akari da abin da ya faru da ita shekara ɗayan da ta gabata, lokacin da hare-haren soji suka kawo cikas ga tattaunawar nukiliya ta Amurka da Iran.

 

 

Advertisement

 

TRT AFRIKA

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending