News
Babban Taron APC: Sani Bello ya kira taron gaggawa

Daga maryam Bashir musa
Sabon Shugaban Kwamitin Riƙo na APC, Gwamnan Jihar Naija, Abubakar Sani Bello, ya kira taron gaggawa na shugabannin jam’iyar na ƙasa.
A wata sanarwar taron da ya sanya wa hannu da kan sa, tare da kuma Ken Nnamani (Kudu-maso-Gabas), Stella Okotete (Shugabar Mata ta Ƙasa), Sanata Aba Ali (Arewa-maso-Yamma) da kuma Farfesa Tahir Mamman (Arewa-maso-Gabas).
A sanarwar, za a yi taron ne ta yanar gizo a ranar 17 ga watan Maris da misalin ƙarfe 11 na safe.
An yanke hukuncin yin taron gaggawar ne a taron kwamitin riƙo km jam’iyar karo na 26 da ya gudana a ranar Talata.
Sanarwar ta ce an kira taron gaggawar ne ta la’akari da sashe na 25B (i da ii) na kundin tsarin mulkin APC da kuma ikon da a ka baiwa Kwamitin Riƙon a taron da a ka cimma matsaya a kan hakan a ranar 8 ga watan Disamba, 2020.