News
Siyasar Kano: Dauda lawan ya ajiye muƙaminsa don takarar ɗan majalisa
Daga muhammad Muhammad zahraddin
Babban mai taimakawa Gwamnan Kano kan ci gaban al’uma Ahmad Dauda Lawan ya ajiye muƙaminsa domin tsayawa takara a zaɓen 2023.
A wata sanarwa da ya fitar, Ahmad Dauda ya ce, ya sauka daga muƙamin ne domin biyayya ga sabuwar dokar zaɓe.
Dauda Lawan ya ce, yana neman ɗan majalisar jihar mai wakiltar ƙaramar hukumar Tarauni.
Wannan dai na zuwa ne kwana guda bayan da Gwamna Ganduje ya bai wa masu riƙe da muƙaman siyasa da ke sha’awar takara umarnin ajiye aiki domin biyayya ga dokar zaɓe.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
