News
2023: Osinbajo Ya Sayi Fom Takararsa A APC Na N100m
Mataimakin Shugaban Kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya sayi fom din takarar Shugabancin Kasa karkashin jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa.
Daya daga cikin jagororin yakin neman zabensa, Sanata Kabiru Gaya ne ya karbi fim din a madadin Osinbajon ranar Alhamis.
Osinbajo dai ya bayyana aniyarsa ta neman takarar a watan Afrilu inda tuni kuma ya dukufa zagayen ji ta bakin daliget-daliget gabanin gudanar da zaben cikin gidan jam’iyar da za ayi a karshen watan Mayu.
Jam’iyyar ta APC dai ta kara kwanaki hudu a wa’adin siyar da fama-faman.
Za a gudanar da zaben fid-da gwanin Shugaban Kasa na jam’iyyar ranar 30 ga watan Mayun 2022.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
