Daga Muhammad Muhammad zahraddin
A Najeriya, mataimakin shugaban kasar Yemi Osinbajo ya sayi fom din na-gani-ina-so da na neman tsayawa takarar mukamin shugaban kasa a inuwar jam’iyya mai mulki ta APC.
Sanata Kabiru Gaya, wanda yana cikin shugabannin ofishin yakin neman zaben Mista Osinbajo ne ya karbi fom din guda biyu a madadin mataimakin shugaban kasar a ranar Alhamis.
Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsaywa takara ne a watan jiya, kuma ya rika zagaya jihohin kasar domin abin da ya kira “tuntubar wakilan jama’a” gabanin zaben fitar-da-gwani da jam’iyyar za ta yi a karshen wannan watan.
Jma’iyyar ta APC ta kara yawan kwanakin sayar da fom din nata da kwanaki hudu.
