Politics
Ana cikin rashin tabbas a jam’iyyar APC
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Kwanaki biyu a gudanar da zaɓen fitar da gwani domin tantace mutumin da zai yi takarar shugaban kasa a APC, rahoton kwamitin tantace masu takara har yanzu bai kammalu ba.
Najeriya ta haramta cin naman daji kan kyandar biri
Wannan na sake tada hankali tsakanin masu neman kujerar shugaban kasa da magoya-bayansu.
Kwamitin da ya tantace masu neman takarar, karkashin jagorancin tsohon shugaban jam’iyyar, Cif John Odigie-Oyegun, ya tantace ‘yan takara 23 a ranar Talata a Abuja.
Tun bayan kammala tantacewar, ake cikin yanayi na ɗar-ɗar tsakanin masu takarar da magoya-baya kan abin da zai iya biyo baya a sakamakon tantacewar.
Sannan akwai rahotanni da ke cewa kwamitin ya karɓi korafi kan jagoran jam’iyyar, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Wannan yanayi na rashin tabbas da ake ciki a APC ya zo daidai da kunnowar sabuwar ɓaraka tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar kan mutumin da zai gaji shugaba Buhari a 2023.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
