Connect with us

News

INEC Ta Tunatar da Jam’iyyun Siyasa Kan Wa’adin Mika Sunayen Yan Takara

Published

on

Daga kabiru badiru fulatan 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya shawarci jam’iyyun siyasa da su kiyaye dangane da wa’adin mika sunayen ‘yan takara a babban zaben 2023.

Farfesa Yakubu ya bayar da shawarar ne a jiya Juma’a a lokacin da ya ziyarci wurin wani taron horo da hukumar ta shirya wa jami’an jam’iyyun siyasa na kasar nan.

Advertisement

 

Taron Horaswar dai zai mayar da hankali ne kan yadda za a yi amfani da sabuwar hanyar mika sunayen yan takara (ICNP) a zaben 2023.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Yakubu, a cewar sanarwar da babban sakataren yada labaran sa, Mista Rotimi Oyekanmi ya fitar, ya ziyarci dukkanin kungiyoyi shida da ake bayar da horon domin tabbatar da cewa jami’an jam’iyyar sun fahimci abin da ake koya musu.

Advertisement

 

Shugaban na INEC ya bukaci jami’an da su lura da su a hankali dangane da ranakun da za su fara aiki da wa’adin ranar da za a fara gabatar da fom din ‘yan takara na zaben kasa da na jihohi zuwa hukumar.

Advertisement

 

Yakubu ya tunatar da jami’an jam’iyyar duk wasu bayanai da ke kunshe a cikin jadawalin ayyuka na babban zabe mai zuwa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending