News
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC tace bata karbi sunan kowane dan takarar gwamna ba daga jam’iyyar PDP a jihar Kano.
Daga kabiru basiru fulatan
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC tace bata karbi sunan kowane dan takarar gwamna ba daga jam’iyyar PDP a jihar Kano.
DSS ta kama wani babban kwamandan ISWAP a Kano
Shugaban hukumar Farfesa Risk uwa ko Arabu Shehu ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Wannan na zuwane bayan yan takarar bangarori biyu na PDP a Kano sun fitar da hotunansu dauke da takaddar dake nuna sune halastattun yan takarar Gwamana a jam’iyyar a lahadinnan.
Bangaren PDP karkashin shugabancin Wada Sagagi da suka zabi Muhammad Sani Abacha da bangaren Aminu Wali da suka Zabi Sadiq Wali dukkaninsu na Ikirarin sune keda halastattun yan takara da zasu tsaya kujerar gwamnna a kakar zabe mai zuwa ta 2023.
To sai dai hukumar zaben mai zaman kanta ta bakin shugabanta na Kano tace har yanzu basu karbi sunan kowanne dan takarar gwamna daga jam’iyyu ba.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
