News
Ɗalibin BUK ya zama shugaban ƙungiyar LAWSAN ta Najeriya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kwamared Yasir Abubakar, ɗalibi mai karantar Shari’a a jami’ar Bayero da ke Kano, kuma ɗan aji 4, ya zama shugaban ƙungiyar ɗalibai lauyoyi ta Najeriya, mai suna LAWSAN.
Hukumar zaben ƙungiyar ta tabbatar da lashe zaɓen da Yasir ya yi bayan ya samu ƙuri’u 30 a zaɓen da aka gudanar a otal ɗin Swiss Spirit Hotel, da ke garin Fatakwal a Juma’ar da ta gabata.
Abubakar dai ya kayar da abokin karawarsa Ann Lyam Iverem daga jami’ar Bingham a jihar Nasarawa, wanda ya sami ƙuri’u 26.
Bayan gudanar da zaɓen, wasu daga cikin mahalarta zaɓen sun nuna murnarsu gami da tabbacin cewa lallai Yasir zai taɓuka abin kirki da yardar Allah.
#TDRHausa
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
