News
A ƙarshe dai Faransa ta amince jirgin ‘yan cirani ya sauka a ƙasar
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Faransa ta amince jirgin ruwan ceto ɗauke da ‘yan cirani da ya taso daga tekun Mediterranean tsayawa a tashar ruwanta, bayan Italiya ta ki amince wa jirgin.
Ministan Harkokin Cikin Gida na Faransa Gerald Darmanin ya ce kin amincewa da Italiya ta yi na tsayawar jirgin rashin imani ne.
Wakilin BBC ya ce ‘yan ciranin sun shafe kwana suna gararamba a teku, daga bisani Italiya ta amince wa jirgi uku tsayawa a tashar ruwanta.
Firaiministar Italiya Georgia Meloni ta ce kalaman ministan cikin gidan Faransa na kin amincewa da ‘yan ciranin rashin tausayi ne.
Jirgin na dauke da sama da ‘yan cirani 200 da suka taso daga Libya.
Advertisements
