News
Yan sandan Kebbi sun ceto mutum bakwai da aka yi garkuwa da su
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Rundunar ‘yan sandan Jihar Kebbi ta ce ta ceto mutum bakwai da aka yi garkuwa da su a garuruwan Bena-Mairairai da Ruwan Kanwa na jihar.
Kwamashinan ‘Yan Sanda Ahmed Magaji Kwantagora ya bayyana yayin taron manema labarai a Birnin-Kebbi cewa ‘yan fashin sun tare hanyar shiga Bena-Mairairai, inda dakarunsa suka yi wa wajen tsinke bayan samun rahoton hakan.
Bayan fafatawa tsakanin ɓangarorin ne kuma aka yi nasarar ceto Jamila Ahamad, da Shamsiya Ahamad, da kuma Tasi’u Haruna.
A wani lamarin daban kuma, kwamashinan ya ce dakarun sun ceto wasu mutum huɗu a yankin Jega da ke jihar waɗanda su ma ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su.
Yayin samamen, ‘yan sanda sun ƙwace mota ƙirar Toyota Corolla daga hannun ‘yan fashin, “sannan an tsaurara sintiri don hana mahara sakat a yankin,” in ji shi.
-
News5 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
