News
Qatar 2022: Zakir Naik Na Halartar Gasar Kofin Duniya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Fitataccen mai wa’azin Musulunci dan kasar Indiya, Dokta Zakir Naik na halartar gasar kwallon kafar na Cin Kofin Duniya da za a soma a Qatar a ranar Lahadi.
Hakan ta bayyana ne bayan fitar hotunan Dokta Zakir Naik bayan saukarsa a filin jirgin sama na Doha, babban birnin kasar Qatar a ranar Asabar.
Yan sandan Kebbi sun ceto mutum bakwai da aka yi garkuwa da su
Zakir Naik ya lashe kyautar Sarki Faisal kan hidima ga Musulunci
Wasu bayanai sun nuna cewa mai Zakir Naik ya je Qatar ne a bisa gayyatar gwamanatin kasar na ya gabatar da wani majalisin wa’azi a yayin da ake gasar.
Qatar ta bijiro da wasu tsare-tsare na yada addinin Musulunci a yayin gasar Cin Kofin Duniya da ake sa ran mutum sama da mutane miliyan biyu da rabi za su halarta.
Wasu daga cikin tsare-tsaren sun hada da samar da wuraren Sallah da kuma wuraren alwala a filayayen wasa, abin da ba a taba yi ba a tarihin gasar a duniya.
Qatar ta kuma hana sayar da barasa a wuraren da za a buga wasannin.
-
News5 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
