Connect with us

News

An Kama Mutum 25 Kan Zargin Yunkurin Kifar Da Gwamnatin Jamus

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

’Yan sanda a Jamus sun kama mutum 25 a fadin kasar da ake zargi da kasancewa mambobi da kuma masu goyon bayan wata kungiyar masu ra’ayin rikau da ke neman hambarar da gwamnatin kasar.

 

Advertisement

Ana dai yi wa kungiyar lakabi da Reichsbuerger, wacce hukumomin kasar ke yi wa kallon ta ta’addanci.

 

Advertisement

Majalisar dattijai ta buƙaci CBN ya yi taka-tsantsan kan ƙayyade cire kuɗi

Bayanai sun nuna ’yan kungiyar na son hambarar da gwamnatin kasar ta karfin tsiya ne domin su dora jagoransu, wanda ke samun tallafi daga kasar Rasha, a matsayin sabon Shugaban Kasar, a cewar Ofishin Babban Mai Shigar da Kara na Kasar.

 

Advertisement

Akalla dai jami’an ’yan sanda 3,000 ne suka gudanar da aikin kamen ranar Laraba a a birane 130 da ke jihohi 11 a fadin kasar.

 

Advertisement

Mai shigar da karar ya ce ana zargin mutanen ne da wani kwakkwaran shiri na kutsa kai ta karfin tsiya zuwa cikin ginin Majalisar Jamus ta hanyar daukar makami.

 

Advertisement

Ofishin ya kuma ce mutum 22 daga cikin wadanda aka kama ’yan asalin kasar ta Jamus ne wadanda ake zargi da shiga kungiyar da aka kira da ta’addanci, yayin da daya daga ciki kuma dan kasar Rasha ne da ake zargi da goyon bayansu.

 

Advertisement

Gidan talabijin na Aljazeera ya rawaito cewa akasarin mutanen da aka kama suna dauke ne da makamai, kuma ana zarginsu da yi wa kasar zagon kasa.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

To sai dai daga bisani a ranar Laraba, gwamnatin Rasha ta musanta hannun kowanne dan kasarta a yunkurin juyin mulkin.

 

Advertisement

“Wannan matsalar cikin gida ce ta Jamus, babu hannun Rasha ko kadan a ciki,” inji Dmitry Peskov, mai magana da yawun fadar gwamnatin kasar ta Kremlin.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending