News
Batun tsaro da tattalin arziki zan sa gaba a Kaduna — Uba Sani
BBC ta tuntubi sabon gwamnan na Kaduna kan abubuwan da al’ummar jihar za su gani bayan rantsar da shi, kuma ya bayyana abubuwa da dama, amma ya fara ne da batun tsaro.
Ya ce, ‘’ Duk abin da ya shafi sha’anin tsaro na al’ummarmu da abin da ya shafi dukiyarsu dole mu tsaya tsayin daka mu ga mun kare su, sannan batun bunkasa tattalin arziki saboda mutane na cikin wani yanayi.”
Sanata Uba Sani, ya ce za kuma su yi ayyuka na ci gaba a kauyuka da bunkasa ilimi da hanyoyi da kuma inganta sana’ar al’umma.
Advertisements
