Connect with us

News

Kano: ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum, Sun Yi Awon-Gaba Da Shanu Sama Da 400 A Gwarzo

Published

on

IMG 20260507 205829 544

Al’ummar yankin Mainika da ke karamar hukumar Gwarzo sun fada cikin jimami bayan wani mummunan hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wasu kauyukan yankin, inda suka kashe mutane tare da sace shanu sama da 400.

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun kai harin ne a kauyukan Gatari, Sara da Dankendi cikin dare, inda suka rika harbe-harbe domin razanar da mazauna yankin kafin su kwashe dimbin dabbobi.

Hadakar Malamai Sun Bukaci A Gudanar Da Siyasar Kano Cikin Lumana

Wata majiya daga yankin ta shaidawa premier Radio cewa harin ya haddasa firgici da tashin hankali, yayin da mazauna kauyukan suka tsere domin neman tsira.

Da safiyar Alhamis aka gudanar da jana’izar marigayi Abdurrazzak mai shekaru kusan 50, wanda ya rasa ransa a yayin harin.

Marigayin ya bar mata biyu masu juna biyu da kuma yara tara, lamarin da ya kara jefa iyalansa da al’ummar yankin cikin alhini.

Advertisement

Al’ummar yankin sun bukaci hukumomin tsaro da gwamnatin jihar da su dauki matakan gaggawa domin dakile hare-haren ‘yan bindiga da ke ci gaba da barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a a yankunan karkarar jihar Kano.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending