News
Kotu Ta Daure Wani Limamin Masallacin Juma’a Wata 1 Kan Tura Bidiyon Tsaraici Ga Matar Aure A Kano
Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Kofar Kudu ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Ustaz Ibrahim Sarki Yola, ta yanke wa wani limamin Juma’a hukuncin ɗaurin wata ɗaya ba tare da zaɓin tara ba, bayan samunsa da laifin tura bidiyon tsaraicinsa ga matar aure ta hanyar WhatsApp.
Freedom Radio ta ruwaito cewa limamin, wanda kuma mai kula da wata makaranta ne a Abuja, ya shiga hannu ne bayan mijin matar ya kai ƙorafi ga jami’an ‘yan sanda, inda ya zarge shi da neman matarsa tsawon kusan shekara guda.
Cutar Sanƙarau Ta Hallaka Yara 33 A Sakkwato
Rahotanni sun nuna cewa wanda aka yankewa hukuncin ya riƙa tura wa matar bidiyoyin tsaraicinsa duk da cewa ta shaida masa tana da aure.
Sai dai duk da hakan, limamin ya ci gaba da matsa mata lamba tare da rokonta da ta amince da buƙatarsa, yana mai cewa bai yarda tana da aure ba.
Bayan gurfanar da shi a gaban kotu da kuma karanta masa tuhume-tuhumen da ake yi masa, ya amsa laifin tare da roƙon kotun ta sassauta masa hukunci.
Daga bisani, Mai Shari’a Ustaz Ibrahim Sarki Yola ya yanke masa hukuncin ɗaurin wata guda ba tare da zaɓin tara ba, domin zama darasi ga masu aikata irin wannan ɗabi’a.
-
News3 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News5 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News4 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
