Connect with us

News

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan tsoffin gwamnonin da ya naɗa ministoci kuma ke amsar fansho

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

Ƙungiyar kare haƙƙin ƴan ƙasa da tabbatar da shugabanci na gari a Najeriya ‘SERAP’ ta kai ƙarar shugaba Bola Tinubu kotu kan gazawar sa wajen hana tsofaffin gwamnonin da suke rike da mukamin minista karbar kudaden fansho na jihohi.

Kungiyar SERAP dai na neman kotu ta tilasta wa Tinubu ya umarci wadannan tsofaffin gwamnonin da su daina karbar irin wadannan kudade.

Advertisement

Kotu ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Zaɓen Gwamnan Jahar Kano

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Lahadi, mataimakin shugaban ƙungiyar a Najeriya, Kolawole Oluwadare, ya ce ministocin da abin ya shafa su ne Nyesom Wike da Bello Matawalle da Adegboyega Oyetola.

Sauran tsofaffin gwamnonin sun hada da Badaru Abubakar da David Umahi da Simon Lalong da Atiku Bagudu da kuma Ibrahim Geidam.

Advertisement

Sanarwar ta ce “Nadin waɗanda ke karbar fansho na rayuwa a matsayin ministoci wani aiki ne na son rai da kuma saɓa wa ƙa’ida.”

“Yayin da da yawa daga cikin ‘yan waɗanda suka ajiye aiki ba a biyan su kuɗaɗen fansho ba, tsofaffin gwamnonin da ke rike da mukamin minista na samun makudan kuɗaɗen alawus-alawus idan sun bar ofis.”

Advertisement

“Gwamnatin Tinubu tana da nauyin hana tsofaffin gwamnonin karbar duk wani hakki na ritaya yayin da suke aiki a matsayin ministoci.”

SERAP dai ta ce wannan dabi’a ba ta dace ba, musamman idan aka yi la’akari da kalubalen tattalin arzikin da ƙasar ke fuskanta.

Advertisement

Sai dai kuma har yanzu ba a sanya ranar fara sauraron karar ba.

Wani labarin kuma Kotu ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Zaɓen Gwamnan Jahar Kano

Advertisement

 

A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.

Advertisement

 

A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.

Advertisement

 

Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.

Advertisement

 

Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending