Connect with us

News

Dakarun Soji Sun Kama Wasu ’Yansanda Bisa Kin Bin Umarnin Shugaba Tinubu Na Janyewa Daga Gadin VIP 

Published

on

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 101 Sun Kama Wasu 182 A Cikin Mako Daya

Rundunar soji ta kama ’yansanda huɗu bisa zargin ci gaba da rakiya ba tare da izini ba ga manyan mutane, lamarin da ya saɓa wa umarnin shugaban ƙasa na janye ’yan sanda daga gadin manyan mutane.

Majiyoyin ’yansanda sun shaida wa Zagazola Makama cewa an kama jami’an ne a ranar 17 ga Disamba da misalin ƙarfe 9:30 na safe, yayin da ake zargin suna bakin aikin rakiyar wani babban mutum.

Advertisement

Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa NIN Ta Zama Lambar Haraji Ga Duk ’Yan Najeriya – FIRS

A cewar majiyoyin tsaro, jami’an soji ne suka kama ’yansandan bayan sun karya umarnin shugaban ƙasa na janye jami’an ’yan sanda daga rakiyar manyan mutane.

Majiyoyin sun ƙara da cewa ’yansandan sun sanya kayan aiki (uniform) masu kama da na Hukumar tsaron farar hula ta kasa (NSCDC), wai domin gujewa ganowa da yaudarar jami’an da ke sa ido kan aiwatar da dokar.

Advertisement

Tun daga lokacin da aka kama su, an tsare jami’an, sannan aka fara matakan ladabtarwa a kansu bisa tanadin ƙa’idojin da ke aiki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending