News
Majalisar Dokokin Kano Ta Soke Dokar Da Ta Kafa Hukumar KNUPDA
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da soke dokar da ta kafa Hukumar Tsarawa da Bunƙasa Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), bayan sabon ƙudirin dokar tsare-tsaren muhalli da kula da bunƙasa gine-gine ya tsallake karatu na uku a zaman Majalisar da aka gudanar ranar Talata.
Zaman ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Jibril Isma’il Falgore, inda ‘yan majalisar suka amince da sabon tsarin da gwamnatin jihar ta gabatar domin sake fasalin yadda ake gudanar da harkokin tsara birane da kula da gine-gine.
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
Da yake yi wa manema labarai bayani bayan zaman, Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar, Hon. Lawan Hussaini Dala, ya ce soke dokar KNUPDA zai bai wa gwamnatin jihar damar kafa sabbin hukumomin bunƙasa birane guda biyu da za su maye gurbin hukumar.
Ya bayyana cewa sabbin hukumomin za su karɓi dukkan ayyukan da KNUPDA ke gudanarwa a baya, kuma za su kasance ƙarƙashin kulawar Ma’aikatar Filaye da Tsare-tsaren Muhalli ta Jihar Kano domin ƙara inganta ayyukan tsara birane da kula da ci gaban gine-gine.
A cewarsa, sabon tsarin zai taimaka wajen magance take dokokin gine-gine, tabbatar da bin ƙa’idojin tsara muhalli, da kuma inganta tsarin bunƙasa birane a faɗin jihar.
Hon. Lawan Hussaini Dala ya ƙara da cewa Majalisar ta amince gwamnatin jihar ta kafa Kano Metropolitan Development Authority (KAMDA) da Kano Area Development Control Authority (KADKA), waɗanda za su maye gurbin KNUPDA wajen gudanar da ayyukan tsara da bunƙasa birane.
Solacebase
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
