News
Shugaba Tinubu ya hana likitoci tafiya hutu ƙetare
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta sanya dokar hana fita hutu ga likitoci da ma’aikatan jinya da sauran ma’aikatan kiwon lafiya da sukan ƙetare zuwa yin hutu a waje.
Ƙaramin Ministan Lafiya, Dokta Tunji Alausa, shi ne ya bayyana haka ranar Asabar a Abeokuta.
Yadda mahara suka sungumi almajirai a Sokoto, kwana biyu bayan jidar ɗalibai 287 a Kaduna
Ya ce daga yanzu, dole ma’aikatan lafiya da ke zuwa ƙetare neman aiki su yi nurabus kafin su tafi.
Ya ƙara da cewa, wannan umarni na ƙunshe ne cikin umarnin da Shugaban Ƙasa Tinubu ya bayar.
A cewarsa, an ɗauki wannan mataki ne domin magance ƙalubalen da ake fuskanta a ɓangaren kula da lafiyar ƙwaƙwalwa.
Kazalika, Ministan ya ce gwamnati ta fara gudanar da shirin ɗaukar sabbin ma’aikata a fannin kiwon lafiya don magance matsalar ƙarancin ma’aikata a ɓangaren.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
