Connect with us

News

Shugaba Tinubu ya hana likitoci tafiya hutu ƙetare

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta sanya dokar hana fita hutu ga likitoci da ma’aikatan jinya da sauran ma’aikatan kiwon lafiya da sukan ƙetare zuwa yin hutu a waje.

Ƙaramin Ministan Lafiya, Dokta Tunji Alausa, shi ne ya bayyana haka ranar Asabar a Abeokuta.

Yadda mahara suka sungumi almajirai a Sokoto, kwana biyu bayan jidar ɗalibai 287 a Kaduna

Ya ce daga yanzu, dole ma’aikatan lafiya da ke zuwa ƙetare neman aiki su yi nurabus kafin su tafi.

Ya ƙara da cewa, wannan umarni na ƙunshe ne cikin umarnin da Shugaban Ƙasa Tinubu ya bayar.

A cewarsa, an ɗauki wannan mataki ne domin magance ƙalubalen da ake fuskanta a ɓangaren kula da lafiyar ƙwaƙwalwa.

Advertisement

Kazalika, Ministan ya ce gwamnati ta fara gudanar da shirin ɗaukar sabbin ma’aikata a fannin kiwon lafiya don magance matsalar ƙarancin ma’aikata a ɓangaren.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending