Connect with us

News

Jami’in Dan Sanda Ya Harbe Alƙali Ana Tsaka Da Shari’ A Kotu

Published

on

DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA 

Wani babban jami’in ‘yan sandan Kenya ya harbi mai jagorantar shari’a a wata kotun majistare da ke Nairobi, babban birnin ƙasar Kenya.

Advertisement

Dan sandan mai muƙamin babban Isfekta ya buɗe wa mai shari’a Monica Kivuti wuta jim kaɗan bayan ta yanke wa matarsa hukunci kan wani laifi da ake zarginta da aikatawa.

Falala Da Abinda Ake Bukatar Musulmi Yayi Ranar ARAFA 

Rahotonni sun ce jami’in ɗan sandan ya fusata ne bayan da kotun ta ƙi amincewa da buƙatar belin matar tasa.

Advertisement

Daga nan ne, Sufeto Samson Kipchirchir Kipruto – wanda ke jagorantar ofishin ‘yan sanda na Londiani da ke yammacin ƙasar – ya zaro bindigarsa tare da harbe alƙaliyar inda ya ji mata rauni.

Nan take kuma jami’an ‘yansanda da ke kotun suka mayar da martani, inda ɗaya daga cikinsu ya harbe tare da kashe mista Kipruto.

Advertisement

Rahoton ‘yan sanda ya nuna cewa uku daga cikin jami’an tsaron da suka mayar da martanin sun samu raunuka a musayar wutar da suka yi da mista Kipruto.

Tuni dai aka garzaya da alƙaliyar da sauran jami’an ‘yan sandan uku zuwa asibiti domin yi musu magani.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending