Connect with us

News

Dole Kowacce Gawa Ta Biya Haraji —Gwamnati

Published

on

Dole Kowacce Gawa Ta Biya HarajiGwamnati

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Gwamnatin Enugu, tayi bayani akan shirin ta na fara karbar haraji akan masu ajiye gawarwaki a dakin ajiye gawa dake fadin Jihar.

Advertisement

A sanarwar da gwamnatin ta fitar tace ba dalilin tattara haraji ne yasa aka kafa dokar biyan kudin ba.

Matsin Rayuwa: Yakamata gwamnatin tarayya ki tausayawa al’umma a rage farashin Fetur – Human Right 

Shugaban hukumar tattara haraji ta Enugu, Emmanuel Nnamani, ne ya sanar da hakan a yau, yayin aikewa da umarnin fara karbar harajin zuwa ga masu Sana’ar adana gawarwaki.

Advertisement

Emmanuel Nnamani, yace tun a baya akwai Wannan doka ba yanzu aka kirkiro ta ba.

A kowacce rana za’a rika biyawa kowacce gawa daya naira 40, sabanin yadda wasu ke cewa dubu 40 za’a biya.

Advertisement

Gwamnatin Enugu, tace masu Sana’ar adana gawarwaki ne zasu rika biyan harajin ba iyalan mamatan da ake ajiyewar ba.

Idan za’a ajiye gawa tsawon kwanaki 100, za’a biya mata naira 4,000.

Advertisement

Emmanuel Nnamani, yace manufar samar da Wannan doka ita ce a tilastawa mutane rage al’adar ajiye gawa ba tare da binne ta ba, wanda hakan ya zama ruwan dare a tsakanin al’ummar Enugu.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending