News
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sace Wata Budurwa Bayan Sun Karɓi Kuɗin Fansa Miliyan 8 A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ƴan bindiga sun kai hari garin Garo da ke Ƙaramar Hukumar Kabo a Jihar Kano cikin daren ranar Lahadi, inda suka sace wata budurwa mai suna Zainab Auwalu, bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan takwas daga hannun mahaifinta.
Zainab, wadda ta kammala makarantar sakandare kwanan nan, an sace ta a gidan mahaifinta.
Ɓarawo Ya Mutu Sakamakon Konewa Da Wutar Lantarki Yayin Da Ya Ke Kokarin Sata A Taransifoma
Ana zargin masu garkuwa da mutane sun kai hari gidan wani fitaccen ɗan kasuwa, Alhaji Auwal, inda suka sace babbar ‘yarsa, Zainab, bayan sun karɓi kuɗi har naira miliyan takwas (₦8,000,000) daga iyalinsa.
Shaidu sun bayyana cewa maharan, kimanin su goma, sun farmaki gidan da misalin ƙarfe 1:20 na dare, inda uku daga cikinsu ke da bindigogi, sauran kuma na ɗauke da makamai daban-daban.
Lamarin ya haifar da firgici a cikin al’umma, inda mazauna yankin ke kira ga mahukunta da su ɗauki matakan magance matsalar rashin tsaro da ke ƙaruwa a yankin.
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da faruwar lamarin, inda mai magana da yawun ta, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da cewa an fara bincike don cafke waɗanda suka aikata lai
fin.”
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
