Connect with us

Sports

Wasu Fusatattu Matasa Sun Kona Alkalin Wasan Ƙwallon ƙafa A Gaban Jama’a

Published

on

sr file 2025 05 07T114824.241
Spread the love

Wasu gungun fusatattun matasa sun yi wa wani mashahurin alkalin wasan ƙwallon ƙafa dukan tsiya tare da ƙonashi da ransa a garin Bukavu da ke gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo.

Alkalin, Patrick Ngalamulume wanda aka fi sani da Ngalas, ya rasu yana da shekaru 36 a duniya.

Zulum Ya Haramta Siyar Da Giya A Borno

Rahotanni sun ce an zarge shi da laifin sata, zargi da ba a gabatar da wata hujja a kai ba.

Advertisement

Lamarin dai ya faru ne a ranar Talata, 6 ga watan Mayu, kuma ya tayar da hankula a yankin, inda jama’a ke bayyana damuwa kan yadda rashin tsaro da kin bin doka da oda ke ƙara kamari.

Kisan gilla da aka yi wa Ngalas ya sake nuna irin mawuyacin halin da ake ciki a gabashin ƙasar, wadda ke fama da rikice-rikice da rashin zaman lafiya tsawon shekaru.

 

Advertisement

 

SAHARA REPORTS

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *