Connect with us

News

’Yan Bindiga Sun Sace Shanu Sama Da 60 A Tsanyawa, Kano

Published

on

FB IMG 1761453622650

Wasu ’yan bindiga masu babura sun kutsa cikin garin Yan Cibi Tsohon Gari a karamar hukumar Tsanyawa, jihar Kano, inda suka sace shanu sama da 60 a daren Asabar.

Wani mazaunin garin da ya bukaci a boye sunansa ya shaida wa Arewa Radio cewa, mazauna da dama sun tsere daga gidajensu saboda tsoro. Ya kara da cewa, ‘yan bindigar sun yi garkuwa da wasu mata, amma daga baya sun sake su bayan sojoji suka isa wurin domin bayar da taimako.

Advertisement

Kungiyar Iyayen Ɗaliban MAAUN Ta Nemi Afuwa Kan Abin Da Ya Faru A Cikin Dakin Jarabawa

Wasu daga cikin mazaunan garin sun ce sun fara shirin barin garin gaba daya saboda tsananin hare-haren.

Garin Yan Cibi Tsohon Gari, dake kan iyaka da jihar Katsina, yana daga cikin yankunan da aka fi samun hare-haren ’yan bindiga a jihar Kano.

Advertisement

Kawo yanzu, hukumomin tsaro ba su fitar da martani kan lamarin ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending