Connect with us

News

‎Na kashe Naira Biliyan 100 Bana Saboda Matsalar Tsaro ‎ ‎ — Gwamnan Borno ‎

Published

on

Gwamnan Jihar Borno dake Najeriya, Babagana Umara Zulum ya ce ya kashe kuɗaɗen da suka kai naira biliyan 100 a jihar sa, a wannan shekarar saboda tinkarar matsalolin tsaro kawai.

‎Zulum ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Sarkin Uba, Ali Ibn Mamza a fadar sa domin yi masa jaje dangane da wasu hare haren da aka kai wa mazauna yankin.

Advertisement

Nuna Bangaranci A Aikin Jarida Da Siyasar Kama Karya Na Kara Ta’azzara – Abdulbaqi Durumin Iya

‎Gwamnan ya kuma yaba wa jami’an tsaro saboda ceto wasu mutane 12 da aka yi garkuwa da su, waɗanda ɗaukacin su manoma ne mata.

‎Zulum ya ce ziyarar ta sa za ta ba shi damar samun cikakkun bayanai da kuma nazarin irin halin da ake ciki a yankin, domin ɗaukar matakan gyara a yankunan Askira da kuma Uba.

Advertisement

‎Gwamnan ya kuma bayyana ɓacin ran sa da yadda matsalar tsaron ke razana ƴan kwangilar da ake bai wa aiki a yankunan.

‎Daga bisani Zulum ya bayyana shirin samar da babbar makaranta da cibiyar zana jarabawar JAMB da asibiti da hanyoyi da kuma wasu kayayyakin more rayuwa a yankin.

Advertisement

‎Zulum wanda ya bayyana muhimmancin tsaro da kuma tasirin sa wajen zaman lafiya, ya bayyana matsalar da yake samu na gina hanyoyi a yankin daga ƴan kwangila, saboda haka ya ce zai samar da wurin fasa duwatsu da kuma sayen motoci 100 na ɗaukar kaya da za’ayi amfani da su wajen gina hanyoyin.

‎Sarkin Uba ya yaba wa gwamnan dangane da ziyarar da kuma ƙoƙarin da ya ke yiwa jama’ar yankin.

Advertisement

 

FRI HAUSA 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending