Connect with us

News

Tinubu, Shettima Za Su Ziyarci Kano Domin Halartar  Tarɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf Zuwa Jam’iyyar APC

Published

on

20230104 182128 e1672910820737 720x430 1

Ana sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima za su ziyarci jihar Kano domin halartar babbar tarba da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta shirya wa Gwamna Abba Kabir Yusuf, bayan sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnoni da manyan jiga-jigan APC daga sassa daban-daban na ƙasar za su halarci taron, wanda ake kallonsa a matsayin muhimmin lamari a siyasar Kano da ma Najeriya baki ɗaya.

Advertisement

Gobara Ta Kone Shaguna 85 A Kasuwar Yan Katako Da Ke Rijiyar Lemo A Kano 

An tsara gudanar da taron ne ranar Litinin, 16 ga Fabrairu, 2026, a Filin Wasanni na Sani Abacha da ke Kofar Mata a birnin Kano. Masu shirya taron sun ce ana sa ran dubban magoya baya da ‘yan siyasa za su hallara.

Advertisement

Wata majiya a jam’iyyar APC ta bayyana taron a matsayin babban mataki ga jam’iyyar a Kano, wadda ake kallonta a matsayin jiha mai tasiri a taswirar siyasar Najeriya. Ta ce taron zai zama wata dama ta nuna ƙarfi da haɗin kai, musamman a yankin Arewa.

An kafa kwamitoci don shirya taron

Advertisement

Masu shirya taron sun ce sun kafa kwamitoci daban-daban domin tabbatar da gudanar da shi cikin tsari, ciki har da kwamitocin tsaro, lafiya da tsabtace muhalli, kula da wurin taro, yaɗa labarai, tsari da ladabi, da kuma wayar da kai da tattara jama’a.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin taron na daga cikin manyan abubuwan da za su ja hankali a Kano a shekarar 2026, duba da irin manyan jiga-jigan da ake sa ran za su halarta.

Advertisement

 

 

Advertisement

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending