News
‘Kano Na Buƙatar Sabbin Ayyuka, Ba Sake Tallata Tsofaffi Ba’ — Tijjani Sarki
Wani mai fafutukar tabbatar da kyakkyawan shugabanci kuma masanin manufofin jama’a, Tijjani Sarki, ya yi kira ga gwamnatoci da su guji jingina wa kansu ayyukan raya ƙasa da gwamnatocin baya suka ƙaddamar, yana mai cewa hakan na iya karkatar da tarihin ci gaban ƙasa.
A wata Samarwa da ya fitar mai taken “History Matters: Development Should Not Be Rebranded”, Tijjani ya ce duk wata gwamnati ta cancanci yabo idan ta kammala ko ta hanzarta aiwatar da ayyukan ci gaba, amma bai dace ta ɗauki cikakken kambun ayyukan da ta gada ba.
Yan Bindiga Sun Tilastawa Mazauna Ƙauyukan Tserewa Daga Gidajensu A Benue
Ya bayyana cewa aikin Kano Northern Bypass an fara shi ne a shekarar 2007 a lokacin gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, yayin da Shirin Ban Ruwa na Bagwai (Watari Irrigation Scheme) ya daɗe yana cikin manyan shirye-shiryen ban ruwa na Jihar Kano.
A cewarsa, idan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ƙara saurin aiwatar da aikin Northern Bypass, hakan abin yabawa ne, amma hakan ba ya nufin ita ce ta assasa aikin.
Tijjani ya ce abin da ya fi ba shi mamaki shi ne yadda wani mai taimaka wa Shugaban Ƙasa ya gabatar da ayyukan Northern Bypass da Bagwai Irrigation Scheme a matsayin sabbin nasarorin gwamnatin Tinubu ba tare da bayyana cewa ayyuka ne da aka gada daga gwamnatocin baya ba.
Ya ce al’ummar Kano na sa ran masu riƙe da muƙaman gwamnatin tarayya daga jihar za su yi amfani da tasirinsu wajen jawo sabbin ayyukan raya ƙasa, maimakon mayar da hankali kan sake tallata tsofaffin ayyuka.
“Abin da zai kasance tarihi mai kyau shi ne samar da sabbin ayyukan tarayya da za su amfani jama’a, ba sake wa ayyukan da aka gada sabon salo ba,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa gwamnati na ƙara samun amincewar jama’a idan ta fito fili ta amince da gudummawar gwamnatocin da suka gabace ta, tare da nuna irin ƙarin ci gaban da ita ta samar.
Sai dai Tijjani ya yaba da shirin Renewed Hope Housing Programme, yana mai cewa shiri ne mai kyau, amma ya ce har yanzu ma’aikata da masu ƙaramin ƙarfi na ci gaba da tambayar ko gidajen da ake ginawa suna cikin ƙarfin aljihunsu.
Ya ƙara da cewa abin da ya fi damunsa shi ne rashin ganin sabbin manyan ayyukan tarayya da jami’an gwamnatin tarayya daga Kano suka jawo zuwa jihar, duk da irin fatan da al’umma suka ɗora a kansu.
A ƙarshe, ya buƙaci jami’an gwamnatin tarayya daga Kano su mayar da hankali wajen samar da sabbin ayyuka a fannonin ban ruwa, albarkatun ruwa, lafiya, ilimi, hanyoyi, wutar lantarki, noma da bunƙasa masana’antu.
Ya ce, “Tarihi yana tunawa da waɗanda suka samar da abin da zai daɗe yana amfani, ba waɗanda suka jingina wa kansu ayyukan da suka gada ba.“
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
