News
Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Sauya Sunan Karamar Hukumar Kunci
Majalisar Dokokin jihar Kano Ta Sauya Sunan Karamar Hukumar Kunci
Hakan na kunshe ne cikin wata takardar da majlisar dokokin jahar Kano ta[wpstatistics stat=usersonline] aikewa ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Kano ranar 14 Ga Watan Disamba.
Tsohon shugaban APC Abdullahi Adamu ya yanke shawarar janyewa daga lamuran siyasa
Jaridar Inda Ranka ta rawaito sanarwar ta kara da cewar majalisar tayi amfani da foka ta 5 ta kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, wanda aka yiwa kwaskwarima, wajen canja sunan karamar Hukumar.
Al’ummar karamar hukumar ta Kunci baya Wanda yanzu suka koma Ghari a yanzu, sun sha kokawa a lokuta Mabambanta kan sunan Karamar hukumar tasu, Inda suka ce yana tasiri wajen hanasu cigaba da kuma jawo musu Kuncin cikin al amu
A wani labarin kuma Tsohon shugaban APC Abdullahi Adamu ya yanke shawarar janyewa daga lamuran siyasa
Yanzu dai Babu wani Abu da al’ummar jihar kano ke yawan tattaunawa akansa Kamar batun shari’ar zaben gwamnan jihar
Wakilin jaridar Inda Ranka Yasir Sani Abdullahi ya gano yadda kusan da yawa daga cikin wuraren zaman alumma da kasuwanni harma da ofisoshin gwamnatin da masu zaman Kansu, Babu wani batu da yafi daukar hankali Kamar batun shari’ar
Magoya bayan dukkan babgarorin manyan jam’iyyun APC Dana NNPP na bugar kirgin samun nasara a kotun koli.
Jam’iyyar APC na da kwarin guiwar cewa Zata Kara samun nasara a kotun koli kasancewar kotun farko da ta biyu duka ta Bata nasara
Sai dai jam’iyyar NNPP Bayan korafe korafe da tayi akan hukunce hukunce na kotun baya, yanzu ta bayyana kwarin guiwar da take dashi na samun nasara a kotun koli
Al’ummar jihar kano da dukkan bangarorin manyan jam’iyyun APC Da NNPP na dakon hukuncin na karshe na kotun koli wadda ake saran Zata yanke cikin karshen watan Nan, shi zai kawo karshen jayayya da kowane bangare keyi a jihar kano
Masu iya magana na cewa Shari’a mace ce da ciki ba’asan wa Zata Haifa ba.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
