News
Gwamnan Ondo, Akeredolu ya rasu Yana da shekaru 67 a duniya.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wata majiya mai tushe ta shaida wa Jaridar SaharaReporters a ranar Laraba cewa Akeredolu ya mutu a Legas.
SaharaReporters ta gano cewa likitocin fadar gwamnatin jihar ne ke kula da shi har zuwa rasuwarsa saboda ba za su iya kai shi kasar waje ba.
Yan Majalissar Dokokin Najeriya Na Shirin Katse Hutu Domin Amincewa Da Kasafin 2024
“Akeredolu ya mutu; ya rasu ne a Legas Yana da shekaru 67 a duniya.,” inji majiyar.
Gwamnan da ke fama da rashin lafiya ya dawo Najeriya a cikin watan Satumba bayan hutun jinya na watanni uku a kasar Jamus, kuma a kwanan baya ya ci gaba da wani taron bayan da shugaba Bola Tinubu ya umarce shi da ya mika mulki ga mataimakinsa Lucky Aiyedatiwa.
Mataimakin sa, Aiyedatiwa ya tsaya a matsayin mukaddashin gwamna.
Bayan dawowarsa Najeriya a watan Satumba, Akeredolu ya zauna a Ibadan, babban birnin jihar Oyo inda ya yi kokarin gudanar da mulkin jiharsa daga can, lamarin da ya janyo cece-ku-ce tsakanin jama’a.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
