News
Kuɗaɗenku ba sa fuskantar haɗari a banki – CBN
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Babban bankin Najeriya, CBN ya bai wa ƴan ƙasar tabbaci cewa kuɗaɗen ajiyarsu da ke asusun bankuna ba sa fuskantar wani haɗari inda ya jaddada samun daidaito a tsarin bankunan ƙasar.
Babban bankin ƙasar ya shawarci jama’a da su ci gaba da haulɗa da bankuna kamar yadda aka saba inda ya nemi ƴan ƙasar su yi watsi da rahotanni marasa tushe game da halin da bankunan ƙasar ke ciki.
Gwamnan Ondo, Akeredolu ya rasu Yana da shekaru 67 a duniya.
Bbc ta ruwaito cewa CBN ya ce yana da dukkan kayan aikin da ake buƙata wajen gudanar da ayyukansa da suka shafi hada-hadar kuɗaɗe.
Wata sanarwa da mai riƙon muƙamin sashen yaɗa labarai na CBN, Hakama Sidi-Ali ta fitar, ta ce “Babban bankin CBN ya ga wasu rahotanni a wasu kafafen yaɗa labarai game da shawarar da aka bai wa gwamnatin tarayya na karɓe iko da wasu cibiyoyin kuɗi ƙarƙashin kulawarsa.
“Bankunan Najeriya suna harkokinsu yadda ya kamata. CBN na shawartar jama’a su ci gaba da tafiyar da harkokinsu ba tare da samun fargaba kan rahotannin da ake yaɗawa ba waɗanda ba daga CBN suka fito ba.” kamar yadda sanarwar ta bayyana.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
